Yansanda Sun Gurfanar Da Kabir Turaki Kan Zargin Bayar Da Bayanan Ƙarya

Rukuni na musamman na jami’an ’yansanda sun gurfanar da tsohon minista kuma shugaban ɗaya daga cikin tsagin jam’iyyar PDP, Kabir Turaki, a gaban babbar kotun Abuja bisa zargin gabatar da bayanan ƙarya.

Fitacciya Ta Rawaito cewa, ana tuhumar Turaki ne da miƙa ƙorafi mai ɗauke da bayanan ƙarya ga Shugaban ’Yansanda na ƙasa a shekarar 2022, lamarin da ya kai ga buɗe wannan shari’a a kansa.

Kamar yadda jaridar Premium Times ta wallafa, Kabir Turaki ya musanta dukkan zargin da ake masa a gaban kotun, inda lauyansa ya nemi a ba shi beli duba da yadda yake mutunta gayyatar kotun a baya.
Alƙalin kotun, Peter Kekemeke, ya amince da buƙatar belin tsohon ministan akan kuɗi naira miliyan ɗari tare da sharaɗin samar da mutum ɗaya amintacce da zai tsaya masa a matsayin lamuni.

Duk da cewa lauyan masu ƙara ya nemi a tsare shi a gidan yari, kotu ta yi watsi da wannan buƙata, inda ta ɗage ci gaba da sauraron shari’ar har zuwa ranar 11 ga watan Yuni domin tantance hujjoji.

Wannan shari’a na zuwa ne a daidai lokacin da jam’iyyar PDP ke cikin rikicin shugabanci wanda ya kai har Kotun Ƙoli, inda Kabir Turaki ke jagorantar ɓangaren da ke fafutukar neman halascin jagorancin jam’iyyar.

Wane tasiri kuke ganin wannan shari'a za ta yi ga martabar Kabir Turaki da kuma ƙoƙarin da yake yi na neman halascin shugabanci a jam'iyyar PDP?

Kuna iya bibiyar shafin Fitacciya Media a Facebook domin samun ingantattun labarai ta wannan mahadin: https://facebook.com/fitacciyamedia

Post a Comment

0 Comments